Daliban Da Aka Sace A Makarantar Kwana Da Ke Kankara A Jihar Katsina A Nigeria Sun Kai Daruruwa
2020-12-14 10:01:56

Majiyar ‘yan sanda ta sanar da cewa; Wasu mutane ne dauke da bindigogin Ak-47 su ka kutsa makarantar kwana dake Kankara da misalin karfe 9;40 inda su ka yi awon gaba da dalibai.
Harin dai ya zo ne a lokacin da shugaban kasar Muhamamdu Buhari
yake ziyara a mahaifarsa ta Daura da ke jihar ta katsina.
Har zuwa yanzu dai jami’an tsaro suna bincike domin gano adadin
daliban da aka yi awon gaba da su.
Wannan harin na ‘yan bindiga yana daga cikin mafi muni da aka
kai a wata makarantar kwana, tun bayan harin da aka kai a garurun Dapchi a 2018
da kuma na Chibok a 2014 a yankin arewa
maso gabashin kasar.
Tags:
daliban da aka sace a makarantar kwana da ke kanka
sun kai daruruwa
shugaban kasar muhamamdu buhari
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!