Ana Ci Gaba Da Samun Koma Bayan Masu Mutuwar Daga Cutar Corona A Iran
2020-12-07 19:38:36

Kakakin ma’aikatar kiwon lafiya ta Iran Sima Sadat Lari, a taron manema labaru da take yi a kowace rana, ta sanar a yau Litinin cewa; A cikin sa’oi 24 da su ka gabata adadin wadanda cutar ta corona ta kashe su ne; 284, da hakan yake nuni da samun koma baya matuka na masu rasa rayukansu.
Daga bullar cutar corona zuwa yanzu dai
ta kashe mutanen da suka kai 50, da 594.
Har ila yau, a cikin wannan tsakanin
mutanen da su ka kamu da cutar su ne dubu 10 da 827. Wadanda suke a kwance a
gadajen asibiti kuwa sun kai 691.
A makwanni kadan da su ka gabata adadin
masu kamuwa da cutar da kuma wadanda ake kwantarwa a gado sun fi haka yawa.
013
Tags:
kakakin ma’aikatar kiwon lafiya ta iran
sima sadat lari
wadanda cutar ta corona ta kashe su ne
284
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!