Yawan Wadanda Suka Mutu Sanadiyyar Turmutsitsi A Najeriya Ya Kara Yawa Zuwa Mutum 32

Yawan mutanen da suka rasa rayukansu a tarayyar Najeriya sanadiyyar tumutsitsi a wasu wuraren raba abinci da kayakin kirsimeta ya karu zuwa 32. Jaridar Daily

Yawan mutanen da suka rasa rayukansu a tarayyar Najeriya sanadiyyar tumutsitsi a wasu wuraren raba abinci da kayakin kirsimeta ya karu zuwa 32.

Jaridar Daily Trust ta Najeriya ta bayyana cewa mutanen 22 suka mutu a turmutsitsin da aka samu a garin Okiji na jihar Anambra a lokacinda wani coci ya bude kofarta don rabawa mutane abinci da kayakin kirsimeti.

Haka ma a birnin Abuja irinsa ya auku inda aka tattaka wasu mutane bayan sun fadi kasa a lokacinda aka bude kofar wani coci don raba abinci da kayakin kirsimeti a garesu kyauta.

Tunji Disa wani jami’in agaji ya fadawa kafafen yadalabarai kan cewa sun dao wasu mutane a wuraren raba abinda, zuwa asbiti, wasu sun rasa rayukansu a yayinda wasu sun sami mummunan raunuka saboda tattakasu da aka yi.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments