Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aikata muggan laifuka da kisan kare dangi kan Falasdinawa a rana ta 444 a jere
Hare-haren wuce gona da iri da sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila suke kai wa Zirin Gaza suka shiga kwana na 444 a jere a safiyar yau Litinin, wanda suke aiwatar da kisan kiyashi kan iyalan Falasdinawa da ‘yan gudun hijira tare da kai hare-hare kan asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya musamman kan shiyar arewacin Zirin na Gaza.
Kafar watsa labaran Falasdinawa ta hanyar yanar gizo na cewa: Majiyoyin kiwon lafiya na Falasdinu sun bayyana cewa, Falasdinawa 50 ne suka yi shahada tare da jikkatan wasu da dama a hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila suka kai kan wasu yankuna a Zirin Gaza tun daga wayewar ranar Lahadi zuwa yau Litinin.
Yayin da ma’aikatar lafiya ta Falasdinu ta watsa rahoton cewa: Adadin Falasdinawa da suka yi shahada sakamakon hare-haren da sojojin mamayar Isra’ila ke ci gaba da kai wa kan Zirin Gaza ya haura zuwa shahidai 45,259, baya ga 107,627 da suka jikkata tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023 miladiyya.
A cewar ma’aikatara lafiyar, ayarin sojojin mamayar Isra’ila sun bude wuta sosai kan asibitin Kamal Adwan da ke aikin yankin Beit Lahiya a arewacin Zirin Gaza.