Masu zanga zanga kimani makunni uku da suka gabata a kasar Libya sun bukaci firai ministan kasar Abdulhamid Dubba ya sauka saboda shi ne ya haddasa rikicin da ya faru a cikin yan makonnin da suka gabata a kasar.
Shafin yanar gizo na labarai Africa News ya bayyana cewa masu zanga zanga kimani 200 sun taro a tsakiyar birnin Tripoli sun rera takin Dole Dubah ya sauka, wanda kuma suna rera wasu taken.
Tun shekara ta 2011 ne a lokacinda kungiyar tsaro ta nato ta goyi bayan yantawaye suka kashe shugaba Kaddafi ne kasar Libya ta rabu gida biyu, bangaren da MDD ta amince da ita a birnin Tripoli da kuma wacce Khalifa Haftar yake jagoranta daga gabacin kasar.