Kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta sanar da kaddamar da hare-hare na musamman guda 10 kan sojojin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila
Kafar yada labaran soji ta kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon ta fitar da takaitaccen bayani kan takamaiman hare-haren da ta kai kan sojojin mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila a kan iyakar kudancin kasar Lebanon a jiya Lahadi. A cikin sanarwar da ta fitar na kunshe da cewa: A ci gaba da goyon bayan al’ummar Falastinu masu tsayin daka a yankin Zirin Gaza da kuma goyon bayan tsayin daka da jajircewa da suke yi, ‘yan gwagwarmaya Lebanon sun kaddamar da wasu jerin hare-hare kan wurare da sansanonin sojin haramtacciyar kasar Isra’ila.