Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sokin Kasar Faransa Kan Mummunar Rawar Da Take Son Takawa Kan Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya soki mummunar rawar da Faransa ke takawa Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya soki kasar Faransa saboda

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya soki mummunar rawar da Faransa ke takawa

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya soki kasar Faransa saboda abin da ya bayyana a matsayin gurgunta rawar da take takawa a kokarin diflomasiyya kan matsayin Shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

A wani rubutu da ya yi a dandalin X, kakakin ya yi tsokaci kan zargin na Faransa, yana mai cewa: Ikirarin da ministan harkokin wajen Faransa ya yi na cewa Iran na daf da kera makamin nukiliya, da’awa ce ta karya kuma marar tushe.

Ya kara da cewa: Wadannan kalamai na karya, tare da barazanar sake kakabawa Iran takunkumi, suna kara karfafa ra’ayin cewa matsayar Faransa na rikidewa zuwa wani matsayi na barna.

Ya ci gaba da cewa: Irin wannan tsarin ba zai karawa Faransa kwarin gwiwa ko matsayinta a Turai ko duniya ba.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments