Iran Da Tajikistan Sun Cimma Yarjeniyoyin Hadin Gwiwa Kan Tattalin Arziki

Kasashen Iran da kuma Tajikistan sun cimma kumshin yarjejeniyoyi 13 na hadin guiwa ta fuskar tattalin arziki. An cimma hakan ne a yayin ganawar da

Kasashen Iran da kuma Tajikistan sun cimma kumshin yarjejeniyoyi 13 na hadin guiwa ta fuskar tattalin arziki.

An cimma hakan ne a yayin ganawar da aka yi a ranar Laraba tsakanin masu fafutukar tattalin arziki daga Iran da Tajikistan din.

An gudanar da taron ne a Dushanbe, babban birnin kasar Tajikistan, tare da halartar ministan al’adu, yawon shakatawa da sana’o’in hannu na Iran, da kuma jami’an Tajik.

A wannan karon, shugaban cibiyar kasuwanci da masana’antu ta kasar Iran Samad Hassan Zadeh, ya jaddada muhimmancin raya dangantakar tattalin arziki a tsakanin kasashen biyu, yana mai nuni da cewa, domin samun saukin kasancewar masu zuba jari na Iran a kasar Tajikistan, ya zama wajibi a warware wasu daga cikinsu.

Samad HassanZadeh ya kuma yi tsokaci kan sana’o’in hannu na Iran, musamman ma kafet, wadanda za su iya taka muhimmiyar rawa a dangantakar kasashen biyu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments