Babban Sakataren MDD Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Biya Rabonsu Na Kudaden Tsaron Kasa Da Kasa

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa karfin bangaren sojojin tabbatar da zaman lafiya na majalisar a duniya, yana dai dai da karfin dukkan

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa karfin bangaren sojojin tabbatar da zaman lafiya na majalisar a duniya, yana dai dai da karfin dukkan kasashen da suke bawa kudaden da ake tafiyar da ayyukansu ne. Don haka ya bukaci kasashen da basu biya rabonsu na kudade karo-karon da ake yi don tafiyar da ayyulan zaman lafiya a duniya bas u yi hakan da gaggawa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto babban sakataren yana fadar haka a jiya talata ya kuma kara da cewa a halin yanzu majalisar tana tafiyar da ayyukan zaman lafiya har 11 a kasashen duniya  wadanda suka hana da  nahiyar Afirka Asia da kuma turai. Guterres ya kara da cewa majalisar tana da sojojin tabbatar da zaman lafiya a kasashen  Congo, Afirka ta tsakiya, Sudan ta Kudu, Lebanon, Cyprus da kuma Kosovo.

Ya ce abinda ake bukata don tafiyar da 9 daga cikin ayyukan tabbatar da zaman lafiya 11 da Majalisar take da su, ya kai dalar Amurka billiyon $5.6 wanda yayi kasa da kasha 8.2% na abinda ta kashe a shekarar da ta gabata.

Labarin ya kara da cewa dukkan kasashen duniya 193,  mambobi a MDD  suna da abinda aka ware mata na kudaden da zata gabatar saboda tabbatar da zaman lafiya a duniya. Guterres ya kammala da cewa MDD ce take gaba a ayyukan tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments