A birnin Roma masu goyon bayan al-ummar Falasdinu sun gudanar da zanga-zanga ta goyon bayan Falasdinawa, sun kuma ya allawadai da kungiyar tarayyar Turai da kuma Amurka kan yadda suka kasance manay-manyan masu taimakawa HKI a kissan kiyashin da take aikatawa a Gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa daubban wadanda suka fito kan tituna a tsakiyar birnin Roma na kasar Italiya suna rera taken ‘Free Free Palastine, wato yanci yanci Falasdinusun kammala ba tare da wata matsala ba.
Amma a jami’ar Colombia ta kasar Amurka rikicin rikicin jami’ar tare da masu goyon bayan kasar Falasdinu ya kaiga, shugabar jami’ar ta yi murabus daga matsayinta, don bada dama ga wani sabon shugaba, wanda zia aiwatar da shirin shugaban kasar Amurka Donal Trump na kawo karshen abinda ya kira ‘kin yahudawa a Jami’ar’.
Ya zuwa yanzu dai shugaban ya yanked alar Amurka miliyon 400 don takurawa shugabancin Jami’ar ta kawo karshen gangamin dalibai da kuma malaman jami’ar suke yin a goyon bayan Falasdinawa da samun yencin kasar.
Har’ila yau da goyon bayan yahudawan sahyoniyya a kissan kiyashin da take yi a kissan kiyashin da takewa al-ummar Falasdinu musamman a Gaza.