Gwamnatin Lebanon Ta Bukaci Majalisar Dinkin Duniya Da Ta Hanzarta Daukan Mataki Kan Isra’ila

Ministan harkokin wajen kasar Labanon ya gargadi kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya kan illar da ke tattare da rashin hukunta haramtacciyar kasar Isra’ila a

Ministan harkokin wajen kasar Labanon ya gargadi kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya kan illar da ke tattare da rashin hukunta haramtacciyar kasar Isra’ila a gaban kuliya

Ministan harkokin wajen kasar Lebanon Abdallah Bouhabib ya yi gargadi a gaban kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa: Babu wanda ke cikin aminci a wannan duniya bayan hare-haren baya-bayan nan da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a Lebanon ta hanyar na’urorin sadarwa na ICOM kirar kasar Japan.

Abdullah Bouhabib ya tabbatar da hakan a jawabin da ya gabatar yayin zaman kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya, yana mai cewa: Idan wannan ta’addancin ya wuce ba tare da la’akari da shi ba a majalisar ta Dinkin Duniya, kuma ba tare da an hukunta haramtacciyar kasar Isra’ila ba, kuma ba a binciko wadanda suka shirya makircin aikata hakan ba, kuma ba a yanke musu hukunci a matsayin hukunta su ba domin tilasta dakatar da ire-iren wadannan hare-haren wuce gona da iri ba, to, lallai al’ummun duniya zasu yi watsi da amincin wannan Majalisar ta kasa da kasa, da kuma nuna ko-o-ho kan batun kare hakki da ‘yancin ɗan adam.

Bou Habib ya ce: Shin wannan ba hakikanin ta’addanci ba ne, yayin da aka kai hari ga duk jama’ar kasa gaba daya, Shin abin da ake bukata ke nan a yau kawar da al’ummar Lebanon baki daya tare da hukunta gaba daya al’ummarta a matsayin hukunci na gama-gari?

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments