An Kashe Jakadan Kasar Italiya A Kasar Demokradiyyar Congo
2021-02-23 08:15:41

A wani hari da aka kai wa tawagar hukumar Abinci dake karkashin MDD, an kashe jakadan na Italiya, mai gadinsa da kuma wani matuki da ke aiki da MDD a gabashin kasar a jiya Litinin.
Wadanda su ka rasa rayukan nasu su
ne;Jakadan na Italiya Luca Attanasio dan shekaru 43, da jami’in tsaro Vittorio
Lcovacci, mai shekaru 30, sai kuma matukun motar hukumar abinci ta duniya da ba
a ambata sunansa ba.
Maharan da su ka bude wuta sun ji wa jakadan raununa da kuma
sauran mutanen da suke tare da shi, sai dai jami’an tsaro sun yi nasarar fitar
da shi zuwa asibitin garin Goma.
Babu kungiyar da ta dauki alhakin kai harin a yankin da yake
kunshe da kungiyoyi masu dauke da makamai.
031
Tags:
an kashe jakadan kasar italiya
a kasar demokradiyyar congo
jakadan na italiya luca attanasio dan shekaru 43
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!