Ana Ci Gaba Da Samun Bayanai Akan Yadda Aka Sace Daliban Makarantar Kwana A Jihar Niger Da Ke Nigeria
2021-02-18 21:55:25

Wani mazaunin daura da makarantar da aka sace yaran ya shaida wa manema labaru cewa; Maharan sun hada yara bibiyu su ka yi musu daurin gwami kafin su yi awon gaba da su.
Daliban
kwalejin kimiyya ta gwamnati a garin Kagara da aka sace, su n kai 27, sai kuma
ma’aikatan makarantar su 15.
Shaidar
ganin idon ya fadawa jaridar Punch ta Nigeria cewa, da misalin karfe 2;00 na
tsakar dare ne maharani da su ke sanye da kakin soja su ka kutsa cikin
makarantar a juya Larabawa.
Wata majiyar
ta shaida wa jaridar cewa; Daya daga cikin daliban mai suna Bejamin Abila ya
gamu da ajalinsa a hannun maharani a yayin da ya yi kokarin daga murya domin
akawo musu dauki.
Tuni dai
gwmanan jihar ta Niger, Abubakar Sani Bello ya bayar da umarnin a rufe wasu
makarantun kwana a cikin kananan hukumomi hudu saboda yadda garkuwar da mutane
ya yawaita a yankunan.
Kananan hukumomin sun kunshi Rafi, Mariga, Munya da Shiroro.
031
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!