Zarif Ya Gana Da Shugaban Kasar Turkiya Rajab Tayyib Erdogan

Ministan
harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jawad Zarif, a daren jiya Juma’a ya gana da shugaban kasar Turkiya Rajab Tayyib
Erdogan a birnin Ankara.
A
cikin wani bayani da ya rubuta a shafinsa na twitter, Zarif ya bayyana cewa, ya
gudanar da tattaunawa mai armashi tare da shugaban kasar Turkiya Rajab Tayyib
Erdogan a kan batutuwa daban-daban, wadanda suka shafi alaka tsakanin Iran da
Turkiya, da kuma sauran batutuwa na yankin da ma na kasa da kasa.
Zarif
gwamnatocin Iran da Turkiya suna da mahanga guda a kan wajabcin yin aiki tare
domin warware matsaloli da suke ci ma al’ummomin yankin tuwo a kwarya, ba tare
da yin katsalandan daga kasashen ketare ba.
Ya ce
kasashen Turkiya da Iran suna yin aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya a
Syria, kamar yadda kuma suna da irin wannan mahangar dangane da abin da ya
shafi yankin Karabakh, inda suka taka muhimmiyar rawa wajen ganin an tsaida
yakin da ya barke tsakanin Azarbeijan da kuma Armenia.
Zarif
ya kammala ziyarar da ya gudanar a cikin wannan mako, wadda ta kunshi kasashen
Azarbeijan, Rasha, Armenia, Georgia da kuma Turkiya.
015