Tsohon shugaban kasar Burundi Buyoya ya rasu bayan fama da cutar Korona

A wata sanarwa da iyalan mamacin suka fitar ta nuna cewa
tsohon shugaban kasar ta Burundi Pierre
Buyoya ya rasu ne a birnin Paris na kasar Faransa bayan ya kamu da cutar korona
Virus yana dan shekaru 71 da haihuwa, mako guda bayan daya sanar da sauka
daga mukamin manzon musamman na kungiyar
AU a kasahena Mali da yankin sahel
Boyoya ya taka muhummiyar rawa wajen tabbatar da mulkin
demukoradiya a karamar kasar ta Afrika, sai dai a ana zarginsa da hannu wajen
kisan da aka yi wa wanda ya gajeshi a mulki, kuma an yanke masa hukunci a baya idonsa
tare da wasu sosjoji guda 20 da fararen hula,
wasu kuma aka yanke musu hukumcin zama
gidan yari na shekaru 20.
Buyoya daya fito daga kabilar tusti ya fara aikin soja ne
kafin daga bisani ya juyin mulki ya dare mulki a shekara ta 1987, kana ya sake zama shugaban kasa bayan wani
juyin mulki da aka yi a shekara ta 1996 suwa 2003
A shekara ta 2000 ya sanya hannun kan yarjejeniyar sulhu a
birnin Arush da ta kawo karshen yakin
basasan kasar da ya jawo rasa rayukan
mutane 300,000 tsakanin shekarata 1993 zuwa 2006 kuma ya sauka daha kan mulkin kasar a shekata
2003 kamar yadda aka kulla yarjejeniya akai.