Search
Close this search box.

Shugaban Aljeriya Ya Koka Kan Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Shugaban kasar Aljeriya ya bayyana cewa: An rusa duk wasu ayyukan bada agajin bil’Adama a Falasdinu Shugaban kasar Aljeriya Abdul-Hamid Taboune ya bukaci dukkanin kungiyoyin

Shugaban kasar Aljeriya ya bayyana cewa: An rusa duk wasu ayyukan bada agajin bil’Adama a Falasdinu

Shugaban kasar Aljeriya Abdul-Hamid Taboune ya bukaci dukkanin kungiyoyin kasa da kasa da cibiyoyin bada agajin bil’Adama da su yi aiki da hakkin da ya rataya a wuyarsu wajen ganin an kawo karshen kisan kiyashin da ake yi wa Falasdinawa musamman al’ummar Zirin Gaza.

Taboune ya jaddada cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa da suke Gaza, don haka dole ne a kan cibiyoyin kasa da kasa su tabbatar an yi aiki da kundin kare hakkin bil’Adama wajen kare Falasdinawa.   

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments