Search
Close this search box.

MDD Ta Nuna Damuwa Akan Yadda Jami’an Tsaron Amurka Suke Amfani Da Karfi A Kan Dalibai Masu Adawa Da Yakin Gaza

Hukumar kare hakkin dan’adam ta MDD ta fitar da bayani a jiya Talata akan yadda jami’an tsaron Amurkan suke amfani da karfi wajen tarwatsa dalibai

Hukumar kare hakkin dan’adam ta MDD ta fitar da bayani a jiya Talata akan yadda jami’an tsaron Amurkan suke amfani da karfi wajen tarwatsa dalibai masu zaman dirshen a harabobin jami’oin kasar.

Shugaban hukumar kare hakkin bil’adam din ta MDD Volker Türk ya bayyana cewa; Da akwai damuwa a cikin yadda aka kama daliban na jami’o’in Amurkan.

Kafafen watsa labarun na Amurkan sun bayyana cewa; ;yan sandan kasar sun rika kwantar da daliban a kasa suna kuma watsa wa wasu barkonon tsohuwa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments