Search
Close this search box.

Amurka Ta Yi Furuci Da Hannu A Kashe Falasdinawa

Shugaban kasar Amurka ya yi furuci da cewa; An yi amfani da makamansu wajen kashe fararen hula a Gaza Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya

Shugaban kasar Amurka ya yi furuci da cewa; An yi amfani da makamansu wajen kashe fararen hula a Gaza

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya amince da cewa: Tabbas an yi amfani da makaman da Amurka ta aike wa gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila wajen aiwatar da kashe-kashen gilla kan fararen hulan Falasdinawa.

Shugaban na Amurka ya kara da cewa: Idan sojojin gwamnatin mamayar yahudawan sahayoniyya suka kai hari kan birnin Rafah yankin da ke da yawan fararen hula, ba za su samu goyon bayan Amurka ba, kuma ba za a tallafa musu da makamai ba, yana mai riya cewa gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ba zata ketara jan layin Amurka kan batun kai hari kan birnin Rafah ba.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments