Aljeriya : Shugaba Abdelmadjid Tebboune Ya Lashe Zaben Kasar Da 94.65 Cikin 100

Shugaban kasar Aljeriya,Abdelmadjid Tebboune, ya sake lashe zaben shugabancin kasar da gagarimin rinjaye. An sake zaben ne a wa’adi na biyu da kashi 94.65% na

Shugaban kasar Aljeriya,Abdelmadjid Tebboune, ya sake lashe zaben shugabancin kasar da gagarimin rinjaye.

An sake zaben ne a wa’adi na biyu da kashi 94.65% na kuri’un da aka kada a zaben da aka gudanar a jiya Asabar.

Daga cikin jimillar kuri’u miliyan 5.6, an zami Abdulmajid Tebboune da kuri’u miliyan 5.320 in ji, shugaban hukumar zaben kasar Mohamed Charfi.

Shugaban hukumar zaben ya sanar a ranar Asabar cewa an samu fitowar masu kada kuri’a da 48.03% “, idan aka kwatanta da 2019 da aka samu kasha (39.83%).  

A waccan zaben, shugaban kasar ya lashe zaben ne da kashi 58% na kuri’un da aka kada.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments