Adadin Falasdinawan Da Isra’ila Ta Kashe A Gaza Ya Kai 40,972

Ma’aikatar lafiya a Gaza ta sanar a ranar Lahadin nan cewa adadin mutanen da sukayi shahada sanadin hare-haren Isra’ila ya kai 40,972 tun bayan fara

Ma’aikatar lafiya a Gaza ta sanar a ranar Lahadin nan cewa adadin mutanen da sukayi shahada sanadin hare-haren Isra’ila ya kai 40,972 tun bayan fara yakin wanda ya shiga wata na goma sha biyu.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, ta ce akalla mutane 33 ne aka kashe a cikin sa’o’i 24 da suka gabata, ta kuma kara da cewa mutane 94,761 ne suka jikkata a zirin Gaza tun daga ranar 7 ga watan Oktoba.

A wani labarin kuma jami’an Isra’ila sun ce an kashe fararen hularta uku a wani hari da aka kai kan iyakar Jordan da Gabar Yamma.

Rahotonni sun ce maharin wanda tuni sojojin Isra’ila suka kashe – direban motar dakon kaya ne, wanda ya taso daga Jordan, sannan ya tsaya a shingen binciken ababen hawa ya kuma bude wuta bayan ya sauko daga motar.

Lamarin ya faru ne a yankin da Isra’ila ke iko da shi, kuma nan ne motocin Jordan dauke da kaya ke bi don shiga Gabar Yamma.

Wannan batu na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da zaman dardar da fargabar barkewar yaki a yankin Gabar ta Tsakiya.

Ko a cikin daren da ya gabata ma an samu musayar hare-haren makamai masu linzami tsakanin Isra’ila da kungiyar Hezbolla ta Lebanon.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments