Kasashen Larabawa Da Dama Sun Marhabin Da Hukuncin Kotun ICC A Kan  Jami’an Isra’ila

Ƙasar Oman a ranar Talata ta yi maraba da matakin da Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya ta ɗauka na ba da sammacin kama Firaiministan

Ƙasar Oman a ranar Talata ta yi maraba da matakin da Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya ta ɗauka na ba da sammacin kama Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu kan zargin aikata laifukan yaƙi.

“Ina maraba da wannan bayyanannen hukuncin na Kotun ICC,” kamar yadda Ministan Harkokin Wajen Oman Badr Albusaidi ya bayyana a shafinsa na X.

“Tarihi zai tuna da masu laifi na ainahi waɗanda suke aikata kisan kiyashi da laifukan yaƙi ga bil’adama. Dole a yi adalci,” kamar yadda ya ƙara da cewa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments