Masu Hannu Da Shuni Sun Yi Alkawarta Samar Da Dala Biliyan 2 Don Taimakawa Gaza

Masu hannu da shuni sun yi alkawarin samar da sama da dala Biliyan biyu don taimakawa zirin Gaza. A yayin taron da aka gudanar na

Masu hannu da shuni sun yi alkawarin samar da sama da dala Biliyan biyu don taimakawa zirin Gaza.

A yayin taron da aka gudanar na masu ba da agaji na kasa da kasa a Kuwait, mahalarta taron sun yi alkawarin samar da wadanan kudaden don taimakawa Gaza.

Taron wanda kungiyar agaji ta Islama ta kasa da kasa (IICO) da ofishin kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya (Ocha) suka shirya, ya tanadi cewa za a raba kudaden ne tsawon shekaru biyu, tare da yiyuwar tsawaitawa, da nufin tallafawa ayyukan jin kai masu muhimmanci a cikin yankin Falasdinawa da aka yiwa kawanya.

Yakin da Isra’ila ta kadammar kan Gaza, bayan harin ba zata da kungiyar Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktoba ya lalata zirin Gaza gabadayansa.

Yakin ya yi sanadin mutuwar falasdinawa kimanin 35,000 wadanda kashi 70 daga cikinsu jarirai ne da yara da mata, sannan sama da mutum dubu 78  da rabi ne suka jikkata.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments