Yan Gudun Hijira 13 Sun Mutu A Tekun Faransa A Lokacind Suke Kokarin Tsallakawa Zuwa Ingila

Yan gudun hijira 13 ne aka tabbatar da mutuwarsu a ranar 3 ga watan satumban da muke ciki bayan da kwalekwalensu ya nutse a kan

Yan gudun hijira 13 ne aka tabbatar da mutuwarsu a ranar 3 ga watan satumban da muke ciki bayan da kwalekwalensu ya nutse a kan hanyarsu ta zuwa ingila daga kasar Faransa ta hanyar ruwa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kwale-kwalen yana dauke da mutane fiye da 61 a lokacinda hatsarin ya auku a arewacin tekun Faransa.

Masu ceto sun ceci mafi yawan yan gudun hijirar da suke cikin kwalekwalen sai dai har yanzun akwai wasu mutane 12 suna jinya a asbitoci a kasar Faransa.

Ministan harkokin cikin gida na kasar Faransa ya bayyana al-amarin a matsayin abin bakinciki, ya kuma ziyarci wadanda abin ya shafa a arewacin kasar Faransa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments