Kungiyar Hizbullahi Ta Mayar Da Martani Kan Hare-Haren Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ta Kai Mata  

Kungiyar Hizbullah ta kai hare-haren daukan fansa kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da suka kai farmaki kan kwarin Beqaa da ke gabashin kasar Labanon Mayakan

Kungiyar Hizbullah ta kai hare-haren daukan fansa kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da suka kai farmaki kan kwarin Beqaa da ke gabashin kasar Labanon

Mayakan kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta kasar Lebanon sun kaddamar da hare-haren daukan fansa ta hanyar harba tarin  makamai masu linzami kan Upper Galilee da yankin Golan na kasar Siriya da aka mamaye, inda ‘yan gwagwarmayar suka fi mayar da martanin kan hedkwatar runduna ta 210 ta Golan da barikin Nafah da kuma hedkwatar rundunar motoci masu sulke na sashin a barikin Yardun.

Sojojin mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi kokarin tunkarar hare-haren domin kakkabo makamai masu linzami na Hizbullah, amma abin ya ci tura, lamarin da ya kai ga barkewar tashin gobara a yankunan da aka kai hare-haren.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments