Daliban Jami’o’i a kasashen duniya da dama suna ci gaba da zanga zangar bukatar a kawo karshen kissan kiyashin da ake wa Falasdinawa a zirin Gaza.
Kamfanin dillancin labaran IRIB-NEWS na kasar Iran ya bayyana cew a jiya Asabar, daliban jami’o’i daban daban a kasar Chille sun fito kan tituna a birane daban daban na kasar, suna kira da a kawo karshen kissan kare dangin da ke faruwa a gaza.
A kasar Jamus kuma wasu daliban jami’o’in sun fito zangfa zangar bukatar a kawo karshen kissan kare dangen da ke faruwa a Gaza, sun kuma bukci gwamnatin kasar Jamus ta dakatar da duk wani tallafin makaman da take bawa HKI, wacce take kashe al-ummar Falasdinu a gaza da su.
Har’ila yau an nakalto labarin bayyana cewa daliban jami’o’ii a biranen Cambera n akasar Australia da kuma da Seul na kasar Korea ta kudu duk sun fito kan titunan kasar suna allawadai da kissan Falasdinawa a Gaza.