An Fara Yin Kira Da Sake Bincike Kan Yadda Aka Kashe Malcolm X
2021-02-22 21:16:59

Dangi da iyalan fitaccen dan
gwagwarmayar kare hakkokin bakaken fata a kasar Amurka Malcolm X sun bukaci da
a sake dawo da batun bincike kan musabbabin kisansa.
Yayin gudanar da wani taron manema labarai a jiya a
taron tunawa da cikar shekaru 55 da kisan mahaifinta, diyar Malcolm X Ilyasa
Al-shabbaz ta bayyana cewa, a matsayinsu an iyalansa, suna bukatar a sake dawo
da batun bincike kan kisan gillar da aka yi masa.
Wannan na zuwa dai bayan samun wasu
bayanai da ke nuni da cewa, akwai hannun jami’an ‘yan sanda na birnin New York
da kuma na hukumar tsaro ta FBI wajen kisan Malcolm X.
Shekaru hamsin da biyar da suka gabata
a ranar 21 Febrairu shekara ta 1965, wasu mutane uku suka bude wutar
bindiga a kan Malcolm X, a lokacin da yake
gabatar da wani jawabi a Audubon a cikin New York.
015
Tags:
dangi da iyalan fitaccen dan gwagwarmaya
dan gwagwarmayar kare hakkokin bakaken fata
kasar amurka
jami’an ‘yan sanda na birnin new york
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!