Kasar Mali Za Ta Bude Tattaunawa Da Masu Ikirarin Jihadi
2021-02-21 08:56:47

Gwamnatin rikon kwarya ta Mali ta sanar da cewa za ta bude tattaunawa da kungiyoyin da suke ikirarin jihadi a kasar.
Pira ministan rikon kwarya na kasar ta Mali Moctar Ouane ya sanar a birnin Bamako cewa; Zai yi matukar kokari domin shirya zabe mai inganci a kasar.
Watanni shida
da su ka gabata ne dai sojoji su ka kifar da gwamnatin kasar Mali, bayan da
kasar ta yi fama da rikice-rikicen siyasa.
Al’ummar
kasar sun rika yin Zanga-zangar ganin an kawo karshen gwamnatin shugaba Bubakar
Keita, wanda a karshe kuwa sojoji su ka hambar da ita.
Mali tana
fama da kungiyoyi masu dauke da makamai
tsakanin masu ikirarin jihadi da kuma masu son ballewa domin kafa kasar
Azbinawa.
031
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!