Pelosi: Wasu Matsoratan ‘Yan Jam’iyyar Republican Suka Ki Yarda A Hukunta Trump

Shugabar majalisar wakilan Amurka Nancy Pelosi ta bayyana cewa, wasu matsorata ne daga cikin ‘yan jam’iyyar Republican suka ki amincewa da a hukunta Donald Trump.
Tashar RT ta bayar da rahoton cewa,
a cikin wani jawabi da ta gabatar a jiya bayan wanke Trump da majalisa ta yi
daga aikata laifin tunzura jama’a domin kai hari kan ginin majalisa, shugabar
majalisar wakilan Amurka Nancy Pelosi ta bayyana cewa, wasu matsorata ne daga
cikin ‘yan jam’iyyar Republican suka ki amincewa da daukar matakin tsige Trump.
Ta ce abin mamaki wasu daga cikin ‘yan
jam’iyyar Republican sun tsaya a gaban majalisa suna kiran Donald Trump mai
laifi, wanda ya cancanci a hukunta shi, amma da aka zo kada kuri’ar hukunta shi
kuma sai suka ja da baya.
Pelosi ta ce irin wadannan ‘yan
majalisa suna tsoron kada su rasa matsayinsu ne, saboda cibiyoyin da suke tsaya
musu wurin zabe da kuma abin da suke samu, wanda kuma suna tsoron rasa hakan.
Trump dai ya tsallake rijiya ta baya
ne bayan da wasu sanatoci ‘yan kalilan suka ki amincewa da a hukunta shi, wanda
hakan ne ya ba shi damar tsallakewa.
015