Kungiyoyin Palasdinawa Sun Bude Tattaunawa Akan Muhimman Batutuwa A Jiya Litinin A Kasar Masar
2021-02-09 09:00:56

Tattaunawar da aka fara a birnin al-kahira za ta shafi muhimman batutuwa da suka hada da yin sulhu a tsakaninsu da kuma yadda za a gudanar da muhimman zabuka.
Muhimman kungiyoyin
Palasdinawa da su ka kunshi Hamas, Jihadul-Islami, PLO da dukkanin kungiyoyin da su ka rattaba hannu
akan yarjejeniyar 2011 suna daga cikin masu halartar taron.
Shugaban kungiyar Hamas,
Isma’ila Haniyyah ya gabatar da jawabi da a ciki ya bayyana cewa; tattaunawar
tana da matukar muhimmanci, kuma ci gaba ne da tattaunawar da aka bude a baya.
Har ila yau Isma’ila
Haniyyah ya ce; Muna sane da yanayi mai hatsari da muke ciki a yanzu na
batutuwan birnin kudus, da hakkin komawa gida, don haka muna da nauyin da ya
rataya a wuyanmu baki daya.
031
Tags:
kungiyoyin palasdinawa
shugaban kungiyar hamas
isma’ila haniyyah
kungiyoyin da su ka rattaba hannu akan yarjejeniya
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!