Iran: Ana Ci Gaba Da Bukukuwan Zagayowar Ranakun Nasarar Juyin Musulunci

A kasar Iran ana ci gaba da gudanar da bukukuwan zagayowar ranakun samun nasarar juyin juya halin muslunci a kasar.
A yau ne aka shiga rana ta biyu da
fara gudanar da tarukan zagayowar ranakun samun nasarar juyin juya halin
muslunci a kasar wanda ya fara daga ranar dawowar marigayi Imam Khomeini a
kasar daga gudun hijira.
Bayan dawowar marigayi Imam Khomeini
a ranar 1 ga watan Janairun 1979 daga
gudun hijirar da ya yi a kasar Faransa, ya sauka a filin sauka da tashin
jiragen sama na Mehrabad da ke birnin Tehran, inda ya gabatar da wani dan
gajeren jawabi ga dubban daruruwan mutanen da suka taru a wurin.
Bayan nan marigayi Imam Khomeini ya
nufi makabartar Beheshti Zahra da ke kudancin birnin Tehran, inda aka bizne
gawawwakin mutanen da suka rasa rayukansu a gwagwarmayar juyin juya halin.
A Beheshti Zahra, marigayi Imam
Khomeini ya gabatar da jawabi mai tsawo, inda ya caccaki gwamnatin sarki Shah,
tare da bayyana cewa tsarin sarauta a matsayin tsarin da ke gudanar da kasa
hakan ya saba wa hankali kuma ba adalci ba ne, domin kuwa al’umma baki daya ba
ta da ta cewa a cikin lamarin tafiyar da kasa.
Ya ce al’ummar Iran suna da hakkin
su zabi irin tsarin da suke so ya tafiyar da kasar, amma dole ne a kawo karshen
tsarin sarauta, wanda zai mayar da sarki shi ne wuka shi ne nama a cikin lamarin kasa da al’umma.
015