Iraki: An Sake Halaka Wani Adadi Mai Yawa Na ‘Yan Ta’adda
2021-01-30 10:02:02

Gwamnatin
Iraki ta sanar da cewa dakarun kasar sun samu nasarar halaka wasu daga cikin ‘yan
ta’addan Daesh a yankin Karku.
Rahotanni daga kasar Iraki na cewa,
a jiya Juma’a dakarun hadin gwaiwa na kasar da suka hada da sojoji da kuma
dakarun sa kai na Hashd Al-shaabi, sun samu nasarar halaka wasu ‘yan ta’addan ashirin
da biyu a farmakin da suke kaddamarwa.
Wannan na zuwa ne a cikin farmakin
da sojoji da kuma dakarun sa kai na kasar suka fara kaddamarwa ne a kan ‘yan
ta’adda da suke neman sake farfadowa a cikin kasar tare da taimakon wasu
kasashen ketare.
Bayan halaka wannan adadi na ‘yan
ta’adda, an kuma samu wasu daga cikin kayayyakin da suke amfani da su wajen kai
hare-haren ta’addanci, da suka hada da bindigogi da kuma nakiyoyi gami da
motoci masu sulke.
015
Tags:
gwamnatin iraki
samu nasarar halaka wasu daga cikin ‘yan ta’adda
fara kaddamarwa
hare-haren ta’addanci
taimakon wasu kasashen ketare
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!