Avril Haynes: Zan Mika Rahoto Kan Masu Hannu A Kisan Jamal Khashoggi

Jami’ar
da za ta rike mukamin babbar darakta ta hukumomin leken asirin kasar Amurka a
gwamnatin Joe Biden Avril Haynes ta bayyana cewa, za ta gabatar da cikakken
bayani kan masu hannu a kisan Jamal Khashoggi.
Tashar
RT ta bayar da rahoton cewa, Avril Haynes ta bayyana cewa, za ta gabatar da
cikakken rahoto kan dukkanin masu hannu a kisan da aka yi wa dan jaridar kasar
Saudiyya Jamal Khashoggi, a cikin cikin ofishin jakadancin kasar ta Saudiyya a
birnin Istanbul na kasar Turkiya a 2018.
Avril
Haynes ta bayyana hakan ne a jiya gaban majalisar dattijan Amurka a lokacin da
take amsa tambayoyi kan lamurra da suka shafi aikin da za a damka mata, inda
sanata Ron Wyden ya tambaye ta kan cewa, shin tana da shirin bayar da
bayanan sirri kan kisan Khashoggi, inda ta amsa da cewa tabbas za ta mika
cikakken rahoto kan hakan.
Ana sa
ran dai rahoton na Avril Haynes wanda za ta mika wa majalisar dattijan Amurka, zai
kunshi wadanda suke da hannu a cikin kisan Jamal Khashoggi, da kuma wanda ya
bayar da umarnin yin hakan, da kuma yadda aka aiwatar da kisan.
Batun
kisan gilar da aka yi Jamal Khashoggi dai yana daya daga cikin batutuwan da aka
yi ta kai ruwa rana a kansu tsakanin Trumkp da ‘yan majalisar dattijai, inda Trump
din yaki amincewa da a mika wa majalisa bayanan sirri kan batun, wanda ake
zargin yariman Saudiyya mai jiran gado Muhammad Bin Salman da hannu kai tsaye
wajen bayar da umarnin yin kisan.
015