Shugaban Tunusiya Ya Buƙaci ‘Yan Kasar Da Su Kawo Ƙarshen Zanga-Zangar Da Suke Yi

Shugaban ƙasar Tunusiya Kais Saied ya buƙaci al’ummar ƙasar da su kawo ƙarshen zanga-zangar da suke yi yana mai kiransu da cewa su yi taka tsantsan kada su bari wasu su yi amfani da matsalolin da suke ciki don cimma manufofinsu na ƙashin kai.
Shugaban
na Tunusiya ya bayyana hakan ne a yau Talata a wata ziyara da ya kai garin
Ariana da ke kusa da birnin Tunis, babban birnin ƙasar, inda cikin jawabin da
yayi ya shaida wa al’ummar ƙasar cewa lalle yana sane da irin talauci da matsin
lambar da al’umma suke ciki, kamar yadda kuma yana sane da waɗanda suke son
amfani da wannan yanayin don cimma manufofinsu. Don haka sai ya buƙaci al’ummar
da su yi taka tsantsan kada su bari wasu su yi amfani da su wajen cimma manufofinsu.
Har
ila yau shugaba Saied ya kirayin ‘yan ƙasar da su guji kai hari kan kadarori na
jama’a da kuma na gwamnati wanda ya ce hakan ya saɓa wa halaye da ɗabi’un
mutanen ƙasar.
Tun
a ranar Juma’ar da ta gabata ce dai mutanen ƙasar Tunusiya a wasu garuruwa na
ƙasar da suka haɗa da Kasserine, Tunis da sauran manyan birane suke ta gudanar
da zanga-zangogi don nuna rashin amincewarsu da yawaitar rashin aikin yi da
kuma matsaloli na tattalin arziki da yayi musu katutu a ƙasar.
Ya
zuwa yanzu dai gwamnati ta tura jami’an tsaro zuwa yankunan da ake tarzomar da
nufin kwantar da ita, inda ya zuwa yanzu an kama wani adadi mai yawa na masu tarzomar.
A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ce dai al’ummar ƙasar Tunusiyan suka gudanar da bukukuwan shekaru 10 da fatattakan tsohon shugaban mulkin kama karya na ƙasar, Zainul Abidin Bin Ali daga ƙasar bayan zanga-zangar da al’ummar ƙasar suka dinga yi don nuna ƙyamar gwamnatinsa.