Masu Kare Hakkin Dan Adam Sun Zargi Faransa Da Kirkiro Dokokin Gallaza Wa Musulmi

Masu kare hakkin bil adama suna
zargin gwamnatin Faransa da kirkiro sabbin dokoki da nufin gallaza wa musulmin
kasar.
A wata zantawa da ya yi da kamfanin
dillancin labaran AFP babban daraktan gudanarwa na kungiyar kare hakkin bil
adama ta Human Rights Watch Kenneth
Roth ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Faransa tana kirkiro sabbin
dokoki wadanda suka yi hannun riga da kare hakkokin dan adam.
Ya ce sabbin dokokin da gwamnatin
Faransa ta gabatar da daftarin kudirinsu a halin yanzu, da sunan sabbin dokokin
tsaron kasa, suna dauke da wasu bangarori wadanda a zahiri ana nufin take
hakkokin musulmi ne a kasar.
Babban daraktan gudanarwa na
kungiyar kare hakkin bil adama ta Human Rights Watch ya ce; gwamnatin Faransa ba
ta yi adalci ba, idan ta yi wa aikin shadanci da kuma imani na akida kudin goro,
domin kuwa bisa dokar kundin tsarin mulkin kasar, dukkanin ‘yan kasa suna
hakkin yin aiki da fahimtarsu ta addini.
Tun bayan zanen batunci kan ma’aiki
da jaridar kasar Faransa ta sake bugawa a watannin baya, wanda ya fuskanci
fushin musulmi a duniya baki daya, gwamnatin Faransa ta gabatar da daftarin
kudirin wasu sabbin dokoki da za su takura wa musulmi, da sunan aikin tabbatar
da tsaron kasa.