Iraki: Za A Aiwatar Da Kudirin Majalisar Dokoki Kan Fitar Da Sojojin Amurka Daga Kasar
2021-01-02 09:19:20

Babban kwamandan dakarun Hashd
Al-shaabi a Iraki Faleh Fayyad ya bayyana cewa, nan da wani dan lokaci mai zuwa
majalisar dokokin kasar Iraki za ta aiwatar da kudirin fitar da sojojin Amurka
daga kasar baki daya.
A wata zantawa da tashar Amasirah,
Faleh Fayyad ya jaddada cewa, babu gudu babu ja da baya dangane da batun
ficewar sojojin Amurka daga Iraki, wanda kuma majalisar ta fitar da wannan
kudiri ne sakamakon kisan Kasim Sulaimani da Abu Mahdi Al-Muhandis da Amurka ta
yi a cikin kasar Iraki.
Ya ce wanann zai wakana nan da ‘yan
kwanaki masu zuwa da yardar Allah, domin hakan shi ne kawai mafita kuma abin da
ya dace da Amurka.
Dangane da alaka tsakanin Iran da
Iraki kuwa, ya bayyana cewa alaka ce mai karfi, wadda babu abin da zai girgiza
ta, kuma bangarorin biyu za su ci gaba da yin aiki tare a dukkanin bangarori.
Tags:
babban kwamandan dakarun hashd al-shaabi
dakarun hashd al-shaabi a iraki
majalisar dokokin kasar iraki
aiwatar da kudirin fitar da sojojin amurka
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!