Kiyayyar Dake Tsakanin ‘Yan Nigeria Ta Yi Yawa Da Bai Kamata Su Rike Makamai Ba
2020-12-31 14:56:52

Wani shugaban al’ummar Iwo a Nigeria kuma basaraken gargajiya, Abiola Ogundokun ne ya bayyana haka, yana mai kara da cewa; Yadda ‘Yan Nigeria ba su ga maciji da juna, ya kamata gwamnati ta hana daidaikun mutane mallakar makamai.
Basaraken ya kara da cewa, bai wa daidaikun mutane lasisin mallakar makamai zai iya jefa kasar cikin hatsaniya fiye da wacce ake da ita yanzu.
Basaraken ya kara da cewa; “Yan Nigeria ba su da isasshiyar
da’ar da za su iya mallakar makamai, saboda kiyayyar da suke yi da juna.
Wani sashe na jawabin Abiola Ogundokun ya bayyana cewa; Da akwai
makirce-makirce da ake kitsawa Nigeria, don haka da akwai bukatar duk masu
hannu da shuni a wajen tafiyar da kasar da su yi namijin kokari domin dawo da
tsaro da zaman lafiya a kasar.
Tags:
kiyayyar dake tsakanin ‘yan nigeria ta yi yawa
bai kamata su rike makamai ba
basaraken gargajiya
abiola ogundokun
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!