Shubaban Kasar Burkina Faso Ya Yi Alakwalin Tabbatar Da Tsaro A Kasar
2020-12-29 15:04:11

Shugaba
Roch Marc Christian Kabore wanda aka sake zabarsa a zango na biyu na
shugabancin kasar ta Burkina Faso, ya ce sake dawo da tsaro a kasar shi ne zai zama abu mafi muhimmanci da
zai sa a gaba.
A jiya
Litinin ne dai Kabore dan shekaru 63 ya yi rantsuwar sake kama aiki na
shugabancin kasar a karo na biyu a cikin filin wasan kwallon kafa na birnin
Ouagadougou.
Shugabannin
kasashen Afirka 10 ne su ka sami halartar binin, da kuma bakin da suka kai
1,200.
Kabore
ya yi furuci da barnar da masu kai hare-hare a kasar su ka yi, wadanda su ka
ketaro daga kasar Mali mai makwabtaka da Burkina Faso.
Akalla
mutane 1,200 ne aka kashe, yayin da wasu miliyan daya su ka yi hijira daga
gidajensu saboda kaucewa fadace-fadace.
013
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!