Ministan Tsaron Kasar Turkiya Ya Ja Kunnen Janar Halifa Haftar Na Kasar Libya Akan Gigin Kai Wa Sojojin Kasar Hari
2020-12-28 08:47:48

Ministan tsaron kasar Turkiya Hulusi Akar wanda ya kai ziyara kasar Libya a jiya Lahadi, ya bayyana cewa; matukar aka kai wa sojojin kasarsa hari to dukkanin cibiyoyin soja da ke gabashin kasar za su zama halartattun wuraren kai wa hari.
Akar wanda ya gabatar da taron manema labaru a birnin Tripoli a jiya Lahadi ya kara da cewa; Babbar matsalar da kasar Libya take fuskanta ita ce ta Halifa Haftar da mutanensa da su ka yi imani da cewa; Dole ne a sauya gwamnati ta hanyar amfani da karfi.
Ziyarar Akar
zuwa Libya ta zo ne bayan da majalisar dokokin kasar Turkiya ta tsawaita wa’adin
sake tura sojojin kasar zuwa Libya na wasu watanni 18 a nan gaba.
Libya ta
fada cikin matsalar tsaro tun bayan da kungiyar yarjejeniyar tsaro ta “NATO” ta
jagoranci kifar da gwamnatin Muammar Gaddafi a 2011.
Kasar mai
arzikin man fetur ta rabe gida biyu a siyasance tsakanin gabashinta da yamma da
ake da gwamnatoci daban-daban da kowane bangare yake samun goyon baya daga
waje.
013
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!