An Yi Harbe-harbe Da Kai Hare-hare A Lokacin Zaben Kasar “Afirka Ta Tsakiya”
2020-12-28 08:44:24

A jiya Lahadi ne aka gabatar da zaben shugaban kasar “Afirka Ta Tsakiya” da kuma na ‘yan majalisar dokoki a cikin tashe-tashen hankula da suka mamaye shi. Shugaban kasar Faustin Archange Touadera ya kada kuri’arsa a karkashin tsaro sojojin Rwanda da kuma dakarun MDD.
Dakarun MDD
sun sanar da cewa sun dakile wani hari da masu dauke da makamai su ka kai a
unguwannin Bria da Paoua da ke cikin babban birnin kasar a yayin da ake gudanar
da zabe.
Kwanakin kadan da su ka gabata, kasashen Rwanda da Rasha sun aike da daruruwan sojojinta zuwa kasar ta “Afrika Ta Tsakiya’ domin dakile wani yunkuri na juyin mulki a yankin Bangui.
013
Tags:
harbe-harbe da kai hare-hare
zaben kasar “afirka ta tsakiya”
shugaban kasar faustin archange touadera
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!