Amurka: An Ga Sassan Jikin Mutum A Wurin Da Aka Kai Hari A Garin Nashville Na Kasar Amurka A Jiya Juma’a
2020-12-26 08:46:12

Kafafen watsa labarun Amurka sun ambato majiyar tsaron kasar tana cewa an sami wasu sassan jikin mutum a wurin da aka kai hari da safiyar jiya Juma’a a tsakiyar garin Nashville da ke jihar Tennessee.
Ya zuwa
yanzu dai jami’an tsaron ba su tantance ko sassan jikin na mutumin da ya kai
harin ne ba, ko kuma na wanda aka kashe
ne.
Da safiyar
jiya Juma’a ta Kirsimeti ne dai wata mota mai makare da abubuwa masu fashewa ta
tarwatse a garin na Nashville da ke jihar Tennessee, tare da jikkata mutane 3
da kuma lalata gidaje 20. Tuni dai hukumar bincike ta ‘yansandan kasar ( FBI)
ta fara gudanar da bincike domin gano hakikanin abinda ya faru.
Masu bincike
sun bayyana cewa ba a taba ganin hari mai girman wanda aka kai jiyan ba, a
cikin kasar ta Amurka.
Tuni dai
hukumar sufurin sana a garin ta dakatar da Zirga-zirga na wani lokaci, saboda
tsinkewar hanyoyin sadarwa a cikin garin.
013
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!