Makaman Tsaron Sama Na Kasar Syria Sun Kakkabo Makamai Masu Linzami Da HKI Ta Harba A Yankin Humah
2020-12-25 19:44:36

Majiyar tsaron kasar Syria ta shaida wa kamfanin dillancin labarun kasar “ SANA” cewa; Da asubahin yau Juma’a ne HKI ta kai hare-hare akan yankin Misyaf da ke gundumar Humah, sai dai makaman tsaron samaniyar kasar ta Syri, sun kakkabo mafi yawancinsu.
Majiyar ta ci gaba da cewa; illar da
hare-haren su ka yi wa yankin ba su da yawa, kuma na ci gaba da tantance su.
Tun da fari wata majiyar tsaro ta
ambaci cewa an ga jiragen yakin HKI suna shawagi a kasa-kasa a saman birnin
Beirut na kasar Lebanon da Jabalu-Lubnan da kuma yankin Matan.
Tun bayan da kasar Syria ta fada
cikin yaki daga 2011, HKI take amfani da halin da kasar take ciki tana kai
hare-hare daga lokaci zuwa lokaci.
A wasu lokuta hare-haren kan haddasa
asara ta rayuka da kuma dukiya.
013
Tags:
kamfanin dillancin labarun “ sana”
makaman tsaron sama na kasar syria
sun kakkabo makamai masu linzami da hki ta harba
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!