MDD : Guteress Ya Yi Kira Ga Duniya Da Ta Ci Gaba Da Alakar Kasuwanci Da Iran
2020-12-19 20:21:29

Babban Magatakardar MDD, Antonio Gutrres wanda yake gabatar da rahoto akan aiki da kudurin MDD mai lamba 2231 na yarjejeniyar Nukiliya ta Iran a 2015, ya bayyana cewa; Kudurin yana yin kira ne ga dukkanin kasashen duniya da su yi aiki da shi.
Antonio
Guterres ya bayyana yarjejeniyar Nukilyar
ta Iran da cewa tana tabbatar da cewa diplomasiyya da tattaunawa sun yi nasara
wajen hana yaduwar makaman Nukiliya.
A wani sashe na rahoton babban magatakardar MDD, ya bayyana takaicinsa akan yadda Amurka ta janye daga yarjejeniyar ta Nukiliya, yana mai cewa; Sake dawo da takunkumin da kwamitin tsaron ya dauke, yana cin karo da kudurin kwamitin tsaro mai lamba 2231.
013
Tags:
babban magatakardar mdd
yarjejeniyar nukiliya ta iran a 2015
ci gaba da alakar kasuwanci da iran
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!