Tsayin Dakan Alummar Iran zai sa Amurka ta Dawo Daga Rakiyar Sanya Mata Takunkumi
2020-12-19 14:58:38

Shugaban kasar Iran Hassan Rohani ya fadi a wajen wani taro
da ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar ta shirya cewa yayi Amanna tsayin
Dakar da Alummar Iran ta nuna a tarihi zai sanya sabuwar gwamnatin Amurka ta
canza tunaninta kan alummar kasar, kuma zai tilasta mata koma kan alkwuran da ta dauka karkashin yaryejejeniyar
nulkiyar da aka cimma matsaya a kai a shekara ta 2015 kuma zai karya takunkumin da ta kakaba
mata.
Gwamnatin Donald
Trumph mai barin gado ta dawo da takunkumin da tsohon shugaban kasar ta Amurka Barack Obama ya daukewa Iran bisa yarjejeniyar
nukiliya da aka cimma tsakanin ta da
sauran kasashe masu karfi na duniya. Kuma ya fice daga yarjejeniyar da aka cimma
matsaya akai rana tsaka.
A nasa bangaren jagoran juyin juya halin musulunci na kasar
Iran Ayatullah sayyid Ali khamina’I ya bukaci kasar da kada ta bata lokaci koda
sa’a daya ne kan batun cire takunkumin makutar hakan zai yi wu ta hanyar da ta
dace da za ta bada tabbacin kare mutunci da martabar kasar
Wannan yana zuwa ne bayan da zababben shugaban Amurka Joe Biden ya bayyana aniyarsa na sake komawa kan yarjejeniyar nukiliyar iran da aka cimma matsaya akai.
Tags:
shugaban kasar iran hassan rohani
ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar
tsohon shugaban kasar ta amurka
zababben shugaban amurka
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!