MDD ta yi Tir da kisan da sojojin Isra’ila suka yi wa wani yaro bapalasdine
2020-12-19 14:29:52

Kwararru kan
kare hakkin bil Adama na Mdd sun bayyana kashe wani Yaro bafalasdine da sojojin HKI
suka yi a matsayin kisan gilla kuma ya keta dokokin kasa da kasa,. kan sun
bukaci da a gudanaar da bincike na musamman mai zaman kasan, game da kisan
gillan da sojojin na HKI suka yi wata matashin bafalasdine mai suna Ali ayman dan shekaru 15 da haihuwa.
Shi dai
wannan matashi an kama shi ne a farkon
watan da muke ciki wajen zanga-zanga a gabar yammacin kogin jodan domin nuna rashin
amincewa da zalunci HKI take yankin
palasdinu ,kuma shi ne yaro na 6 da sojojin HKI suka kashe a wannan shekarar
mai karewa ta 2020,
Maa’aikatar
watsa labarai ta palasdinu ta zargi sojojin HKI da kashe yara matasa da gangan,
ya kara da cewa kimanin matasa 3097 ne suka rasa rayuwakansu a hannun sojojin
HKI daga lokacin da aka fara zanga
zangar intifada a shekara ta 2000 zuwa yanzu.
Sai dai duk da tofin Allah tsine da kasashen duniya ke yi game da kashe yara da mata da sojojin HKI suke yi wannan bai hana gwamnatin Isra’ila ci gaba da yin kisan gilla kan yara kanana palasdinwa da take yi ba.
Tags:
kwararru kan kare hakkin bil adama
wani yaro bafalasdine
gudanaar da bincike
gabar yammacin kogin jodan
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!