Iran Ta Kira Yi Amurka Da Ta Janye Sojojinta Daga Kasar Syria
2020-12-17 13:58:35

Jakadan Iran a MDD Majid Takht-Ravanchi wanda ya yi bayani yadda kasarta ta taimakawa gwmanati da al’ummar Syria wajen fada da ayyukan ta’adanci, ya yi kira ga Amurka da ta janye sojojin da ta girke a kasar.
Takht-Ravanchi, wanda ya ke gabatar da jawabi
a wurin taron da kwamitin tsaron MDD ya shirya dangane da; Halin da Syria take
ciki ta fuskokin tsaro da yanayin
rayuwar al’ummar kasar, ya ci gaba da cewa; Wajibi ne ga dukkanin duniya da ta
girmama hurumin kasar Syria da cin gashin kanta da ‘yancinta na siyasa.
Har ila yau jakadan na Iran a MDD ya ce; Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana cikin shirin bayar da gudunmawa domin samo mafita akan rikicin kasar Syria.
013
Comments(0)
Success!
Error! Error occured!